fidelitybank

Kotu ta hana Anyanwu bayyana kansa a matsayin sakataren jam’iyyar PDP

Date:

Wata babbar kotun birnin tarayya Abuja, ta umurci Sanata Samuel Anyanwu da ya daina bayyana kansa a matsayin sakataren jam’iyyar PDP na kasa.

Umurnin dai ya biyo bayan karar ne da ke neman a ba wa jam’iyyar PDP izinin amincewa da Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar na kasa har sai an yanke hukunci kan karar.

Kotun mai lamba FCT/HC/M/015/23 tana da Douglas Nwachukwu a matsayin wanda ya shigar da kara, yayin da PDP, Anyanwu da kuma hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, aka saka sunayen wadanda ake kara.

Bayan sauraron karar F. S. Jimba, lauyan mai kara, Mai shari’a M.M Adamu ya hana Anyanwu bayyana kansa a matsayin sakataren jam’iyyar PDP na kasa.

Adamu ya kuma hana PDP da INEC amincewa da Anyanwu a matsayin sakataren kasa har sai an yanke hukunci.

An dage sauraren karar zuwa ranar 24 ga watan Janairu, 2024 domin sauraron karar.

DAILY POST ta ruwaito Anyanwu shine dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a zaben da aka kammala a jihar Imo amma ya sha kaye a hannun dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Hope Uzodinma.

Duk da haka, ya koma ofishin sa a matsayin Sakatare na kasa a sakatariyar jam’iyyar ta kasa ranar Talata.

DAILY POST ta tuna cewa wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun bukaci ya yi murabus a matsayin sakataren kasa kafin zaben na ranar Asabar.

Da yake jawabi ga ma’aikatan sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa a ranar Talata, Anyanwu ya godewa ‘ya’yan jam’iyyar bisa goyon bayan da suka bayar a lokacin zaben.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp