fidelitybank

Kotu ta hana a kama mai magana da yawun Gwamnan Kano

Date:

Babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin hana Sufeton ‘yan Sanda (IGP), DSS, da sauran hukumomin tsaro kama Malam Sanusi Bature Dawakin-Tofa, mai magana da yawun gwamna Abba Kabir Yusuf.

Kotun ta bayar da wannan umarnin a ranar 12 ga Disamba, 2024, wanda ke kare Dawakin-Tofa daga “kame ko tsarewa, da tsoratarwa” daga IGP, DSS, da sauran hukumomin tsaro.

An kuma fadada wannan umarni zuwa ga mataimakin Sufeton ‘yan Sanda (AIG) na zone 1, kwamishinan ‘yan sanda na Kano, SP Mojirade Obisiji, DCP Akin Fakorede, hukumar tsaro ta NSCDC da sauransu.

Wannan kariya ta shari’a ta biyo bayan zargin da Dr Abdullahi Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya yi cewa Dawakin-Tofa shi ne ya kitsa dakatar da shi a matakin mazabar APC watanni shida da suka wuce.

Rikicin ya fara ne bayan Ganduje ya yi zargin cewa akwai wani tuggu da Dawakin-Tofa, wanda suke mazaba daya, da kuma gwamnatin juhar Kano karkashin jagorancin NNPP suka kitsa.

Ganduje ya bayyana cewa wannan mataki na dakatar da shi wani yunkuri ne na rage tasirinsa a siyasa.

Biyo bayan korafin Ganduje, IGP ya gayyaci Dawakin-Tofa zuwa Abuja tare da shugabannin mazabar APC na Ganduje, inda aka yi masa zargin kulla tuggu da aikata abubuwan da ka iya haddasa rashin zaman lafiya.

Wannan rikici, wanda ya samo asali daga takaddamar siyasa tsakanin manyan jiga-jigan siyasar Kano guda biyu, ya kara ta’azzara dangantakar da ke tsakanin Ganduje da gwamna Yusuf.

Dawakin-Tofa, ta bakin lauyoyinsa karkashin jagorancin Barr. Haruna Musa Muhammad, ya kalubalanci wannan gayyata ta hanyar kai kara gaban kotu, yana mai bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na siyasa don bata masa suna da kuma hana shi gudanar da aikinsa.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp