fidelitybank

Kotu ta hana a kama mai magana da yawun Gwamnan Kano

Date:

Babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin hana Sufeton ‘yan Sanda (IGP), DSS, da sauran hukumomin tsaro kama Malam Sanusi Bature Dawakin-Tofa, mai magana da yawun gwamna Abba Kabir Yusuf.

Kotun ta bayar da wannan umarnin a ranar 12 ga Disamba, 2024, wanda ke kare Dawakin-Tofa daga “kame ko tsarewa, da tsoratarwa” daga IGP, DSS, da sauran hukumomin tsaro.

An kuma fadada wannan umarni zuwa ga mataimakin Sufeton ‘yan Sanda (AIG) na zone 1, kwamishinan ‘yan sanda na Kano, SP Mojirade Obisiji, DCP Akin Fakorede, hukumar tsaro ta NSCDC da sauransu.

Wannan kariya ta shari’a ta biyo bayan zargin da Dr Abdullahi Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya yi cewa Dawakin-Tofa shi ne ya kitsa dakatar da shi a matakin mazabar APC watanni shida da suka wuce.

Rikicin ya fara ne bayan Ganduje ya yi zargin cewa akwai wani tuggu da Dawakin-Tofa, wanda suke mazaba daya, da kuma gwamnatin juhar Kano karkashin jagorancin NNPP suka kitsa.

Ganduje ya bayyana cewa wannan mataki na dakatar da shi wani yunkuri ne na rage tasirinsa a siyasa.

Biyo bayan korafin Ganduje, IGP ya gayyaci Dawakin-Tofa zuwa Abuja tare da shugabannin mazabar APC na Ganduje, inda aka yi masa zargin kulla tuggu da aikata abubuwan da ka iya haddasa rashin zaman lafiya.

Wannan rikici, wanda ya samo asali daga takaddamar siyasa tsakanin manyan jiga-jigan siyasar Kano guda biyu, ya kara ta’azzara dangantakar da ke tsakanin Ganduje da gwamna Yusuf.

Dawakin-Tofa, ta bakin lauyoyinsa karkashin jagorancin Barr. Haruna Musa Muhammad, ya kalubalanci wannan gayyata ta hanyar kai kara gaban kotu, yana mai bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na siyasa don bata masa suna da kuma hana shi gudanar da aikinsa.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp