fidelitybank

Kotu ta fara sauraron karar mutumin da ake zargi da kashe dan uwansa a Kano

Date:

Wata kotun majistare da ke zamanta a Kano, a ranar Laraba, ta bayar da umarnin tsare wani mutum mai shekaru 37, Jamilu Ahmed, a gidan gyaran hali, bisa zarginsa da dukan kaninsa, Alhassan, mai shekaru 30 har lahira.

Lauyan masu gabatar da kara, Aminu Dandago, ya shaida wa kotun cewa Ahmed ya aikata laifin ne a ranar 13 ga Fabrairu, 2022 a Chediyar Kuda Quarters Kano.

Dandago ya yi zargin cewa a daidai wannan rana da misalin karfe 10 na dare Ahmed ya yi ta bugun kanin nasa akai-akai a cikin rashin fahimta.

Ya ce marigayin ya samu raunuka a ciki kuma an kai shi Asibitin kwararru na Murtala Muhammad Kano inda aka tabbatar da rasuwarsa a lokacin da yake karbar kulawa.

Laifin, in ji mai gabatar da kara, ya saba wa tanadin sashe na 221 na kundin laifuffuka.

Alkalin kotun Farouk Ibrahim-Umar, bai karbi rokon Ahmed ba.

Ibrahim-Umar ya umurci ‘yan sanda da su mayar da fayil din karar ga daraktan kararrakin jama’a na jihar Kano domin samun shawarar lauya.

Ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 8 ga watan Satumba

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp