fidelitybank

Kotu ta daure Matasan da suka daki jami’an KARROTA

Date:

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano, wato KAROTA, ta gurfanar da wasu mutane uku da ake zargi da cin zarafin jami’anta yayin da suke gudanar da aikinsu.

An gurfanar da mutanen da suka hadar da Abubakar Mustapha, Najib Idris, da Faruq Dan Alhaji a gaban kotun Noman Islands mai lamba 47, dake Sabon Gari.

A yayin zaman kotun, alkalin ya karanto musu tuhumar da ake yi, wanda ya hada da hana jami’an gwamnati gudanar da aikinsu, wanda ya saba da sashe na 79, 171, 242, da 327 na kundin penal code.

Biyu daga cikin wadanda ake zargin, wato Abubakar Mustapha da Najib Idris, sun gurfana a kotu, inda aka tura su gidan yari har zuwa lokacin da za a kammala shari’a. Sai dai kotu ta bayar da umarnin kamo Faruq Dan Alhaji, wanda yanzu haka ya tsere.

Alkalin kotun ya yi gargadi ga jama’a da su guji aikata irin wannan abu ga jami’an tsaro. Haka zalika, ya shawarci jami’an KAROTA da su yi aiki da kwarewa da ladabi yayin da suke gudanar da ayyukansu, kamar yadda dokokin hukumar suka tanada.

A nasa bangaren, shugaban hukumar KAROTA, Faisal Mahmud Kabir, ya nuna jin dadinsa da yadda shari’ar ta gudana. Ya kuma yi kira ga jama’a da su guji daukar doka a hannunsu idan sun samu sabani da jami’an hukumar.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp