Kotun Shari’ar muslunci mai zamanta a yankin Ungogo karkashin mai shari’a, Mansur Ibrahim, ta hori wasu matasa har su 5 da daurin shekara 2 kowannen su.
Tun da farko kotun ta samu matasan da laifin boye wasu ‘yan mata uku ta hanyar yin ikirari da bakinsu.
Mai gabatar da kara ya shaidawa kotun cewar, laifin ya saba da sashi na 341 na shari’a penal code na shekarar 2000.
Mai shari’a, Mansur Ibrahim, ya bayyana cewar, a laifin hada baki ya daure su har tsawon shekara daya ko zabin tara na dubu 20, sai kuma laifin boye mutane, shi kuma shekara daya babu zabin tara.
Matasan sun hadar da Jamilu Musa da Abdullahi Magaji da Janaidu Abubakar da Adamu Sani da kuma Hafizu Surajo.