Wata Kotun Majistare da ke Kano a ranar Juma’a ta bayar da umarnin tsare wasu mutane uku, Abba Aminu mai shekaru 27, Hashimu Lawan mai shekaru 29 da Abubakar Mukhtar mai shekaru 25 a gidan yari, bisa zargin mallakar muggan makamai.
Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da wadanda ake zargin da laifin hada baki, yunkurin aikata laifin: yin fashi da makami, da kuma mallakar muggan makamai.
Alkalin kotun, Mustapha Sa’ad-Datti, ya bayar da umarnin a tasa keyar wadanda ake zargin zuwa wani gidan gyaran hali.
Ya umurci ‘yan sanda da su mayar da fayil din karar zuwa ofishin kula da kararrakin jama’a (DPP) domin samun shawarar lauya.
Sa’ad-Datti ya dage sauraron karar zuwa ranar 14 ga watan Fabrairu domin sauraren karar.
Tun da farko lauya mai shigar da kara, Miss Asma’u Ado, ta shaida wa kotun cewa wadanda ake zargin sun aikata laifin ne a ranar 5 ga Satumba, 2022, a gidan Zoo Road Quarters, Kano.
Ado ya yi zargin cewa wadanda ake zargin, a wannan rana da misalin karfe 1:30 na safe ‘yan sanda sun kama su ne a lokacin da suke aikin sa ido, kuma an same su da dogayen wukake masu kaifi guda uku da laya.
Ta ce laifin ya ci karo da sashe na 97,95, da na 103 na kundin laifuffuka.
Sai dai wadanda ake zargin sun musanta aikata laifin.