fidelitybank

Kotu ta daure Limami saboda ya kashe Alade

Date:

Wata kotu a Rwanda ta daure wani malamin addinin Islama har na tsawon shekara biyar a kurkuku saboda ya kashe wani alade a harabar wani masallaci.

Wasu shaidu uku sun shaida wa kotun cea sun ga limamin mai suna Sadate Musengimana yana dukan aladen da wani katako matakin da ya kashe shi nan take.

Sai dai lauyansa ya shaida wa kotun cewa ba da gangar ya kashe aladen ba, yana cewa ya yi kokarin koran shi daga harabar wani masallaci da ke gundumar Kayonzo a gabashin kasar ne cikin watan Fabrairu.

“Da yaji yara na cewa wani alade ya shiga masallacin, sai ya fito da wata sanda domin ya kore shi. Ya daki aladen kuma ya mutu, amma bai yi niyyar kashe shi ba,” kamar yadda lauyansa Yusuf Nsengiyumva ya shaida wa BBC.

Lauyan ya ce ya daukaka kara kan wannan hukuncin “mai tsanani”.

Tun watan Fabrairu ake tsare da Liman Musengimana, watan da ya kashe aladen.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp