fidelitybank

Kotu ta daure Birkiloli biyu da zargin satar wayar lantarki

Date:

A ranar Laraba ne wata kotun karamar hukumar Karu da ke Abuja, ta bayar da umarnin a tsare wasu leburori biyu a gidan gyaran hali, bisa zarginsu da satar igiyoyi masu sulke na wutar lantarki.

‘Yan sandan sun tuhumi Nature Mark mai shekaru 27 da Gabriel Sebastian mai shekaru 22, da laifin hada baki, barna da kuma sata.

Alkalin kotun, Mista Hassan Mohammed, ya dage bayar da belin wadanda ake kara sannan ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 16 ga watan Disamba domin sauraren karar.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan gyaran hali na Keffi a jihar Nasarawa har sai an kammala binciken da ‘yan sanda za su gudanar.

Tun da farko, Lauyan masu shigar da kara, Mista Olanrewaju Osho, ya shaida wa kotun cewa, babban jami’in tsaro na kamfanin gine-gine na ENL da ke Guzape, Abuja ne ya kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sanda na Asokoro.

Osho ya shaida wa kotun cewa a ranar 8 ga watan Nuwamba, an kama wadanda ake tuhuma da igiyoyin sulke na kamfanin.

Laifin a cewarsa ya sabawa tanadin sashe na 97, 327 da 288 na penal code.
Wadanda ake tuhumar dai sun musanta aikata laifin.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp