fidelitybank

Kotu ta dakatar da wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290

Date:

Kotu da dakatar da wa’adin da Najeriya ta bai wai kamfanin Meta, mallakin Facebook da Instagram da WhatsApp, na biyan tarar dala miliyan 290 bayan da kamfanin ya shigar da ƙorafi a kotu, wanda hakan ya dakatar da wa’adin biyan tarar.

Tun da farko, hukumar sanya ido kan gogayya tsakanin kamfanoni da kuma kare haƙƙin masu sayen kayayyaki (FCCPC) ta sanya wa Meta wa’adin 30 ga Yuni, 2025, domin biyan tarar da aka kakaba masa bayan samun shi da laifin taka dokokin da suka jiɓanci gasa da tallan haja da kuma na bayanan sirri.

Sai dai FCCPC ta tabbatar wa BBC cewa Meta ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin a kotun daukaka ƙara.

Kamfanin Meta ya kuma nemi a dakatar da aiwatar da hukuncin har zuwa lokacin da kotu za ta yanke shawara.

A watan Mayu ne kamfanin na Meta mamallakin Facebook ya yi barazanar rufe ayyukansa a Najeriya bisa abin da ya bayyana da tarar da ta wuce hankali.

Wani rahoto ya nuna cewa al’ummar Najeriya ka iya rasa damar ci gaba da hulɗa da shafukan Facebook da Instagram idan dai har kamfanin na Meta ya aiwatar da barazanar da ya yi na rufe ayyukan nasa a ƙasar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp