fidelitybank

Kotu ta dage yanke hukunci kan sauya shekar Ayade daga PDP zuwa APC

Date:

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage yanke hukunci kan karar da ake zargin ta kori Ben Ayade a matsayin gwamnan jihar Cross River.

Jam’iyyar PDP ce ta shigar da karar da ke neman a tsige Ayade daga mukaminsa biyo bayan sauya sheka da Gwamna ya yi zuwa jam’iyyar APC.

Wanda ya hada da mataimakin gwamnan Cross River, Ivana Ejemot Esu.

Lauyan PDP Emmanuel Ukala (SAN) ne ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS/975/2021.

Mai shari’a Taiwo Taiwo ya sanya yau don yanke hukunci kan makomar Ayade’a a matsayin gwamnan Cross River.

Sai dai a cewar jaridar The Nation, kotun ta sanya ranar 6 ga Afrilu, 2022, a matsayin sabuwar ranar da za ta ci gaba da sauraren karar da ke neman tsige Ayade daga mukaminsa.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata ne aka kori ‘yan majalisar dokokin jihar Cross River 20 saboda sun fice daga PDP zuwa APC.

Mai shari’a Taiwo Taiwo na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ya kori ‘yan majalisar a wani hukunci da ya yanke ranar Litinin, kamar yadda kafar yada labarai ta Naija ta ruwaito.

Alkalin kotun ya ce ‘yan majalisar su bar kujerunsu bayan sun yi watsi da jam’iyyar da ta kai su karagar mulki.

Mai shari’a Taiwo, ya umarci kakakin majalisar da sauran ‘yan majalisar da suka sauya sheka daga PDP zuwa APC da su gaggauta barin kujerunsu.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp