fidelitybank

Kotu ta dage shari’ar da ake tuhumar Nnamdi Kanu har sai yadda hali ya yi

Date:

Babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, ta ɗage sauraron shari’ar da ake yi wa shugaban ƙungiyar masu rajin kafa ƙasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu.

Ana tuhumar Kanu da laifuka da dama, waɗanda suka jiɓanci ta’addanci, tun bayan kama shi da kuma mayar da shi Najeriya a watan Yunin 2021.

Tun a wancan lokacin ake ci gaba da tsare jagoran na IPOB, kuma duk wani yunƙuri na neman beli ya ci tura.

A baya an samu tsaiko wajen ci gaba da shari’ar bayan da Mista Kanu ya buƙaci mai sauraron ƙarar, Binta Nyako ta tsame kanta daga shari’ar kasancewar “ba ya da ƙwarin gwiwa a kan ta.”

Nyako ta sanar cewa ta tsame kanta daga shari’ar. To sai dai babban alƙalin kotun ya sake mayar wa alƙaliyar takardun shari’ar domin ta ci gaba da jan ragamarta, kasancewar Nnamdi Kanu bai gabatar da buƙatar tasa a rubuce ba.

A zaman na yau Litini, mai shari’a Binta Nyako ta ce babban alƙalin kotun bai amince da janyewar tata ba.

Ta kuma buƙaci masu kare Kanu da su gabatar da buƙatarsu a rubuce, matuƙar suna nan a kan bakarsu ta cewa sai ta tsame kanta daga shari’ar.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp