fidelitybank

Kotu ta dage shari’ar da ake tuhumar Nnamdi Kanu har sai yadda hali ya yi

Date:

Babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, ta ɗage sauraron shari’ar da ake yi wa shugaban ƙungiyar masu rajin kafa ƙasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu.

Ana tuhumar Kanu da laifuka da dama, waɗanda suka jiɓanci ta’addanci, tun bayan kama shi da kuma mayar da shi Najeriya a watan Yunin 2021.

Tun a wancan lokacin ake ci gaba da tsare jagoran na IPOB, kuma duk wani yunƙuri na neman beli ya ci tura.

A baya an samu tsaiko wajen ci gaba da shari’ar bayan da Mista Kanu ya buƙaci mai sauraron ƙarar, Binta Nyako ta tsame kanta daga shari’ar kasancewar “ba ya da ƙwarin gwiwa a kan ta.”

Nyako ta sanar cewa ta tsame kanta daga shari’ar. To sai dai babban alƙalin kotun ya sake mayar wa alƙaliyar takardun shari’ar domin ta ci gaba da jan ragamarta, kasancewar Nnamdi Kanu bai gabatar da buƙatar tasa a rubuce ba.

A zaman na yau Litini, mai shari’a Binta Nyako ta ce babban alƙalin kotun bai amince da janyewar tata ba.

Ta kuma buƙaci masu kare Kanu da su gabatar da buƙatarsu a rubuce, matuƙar suna nan a kan bakarsu ta cewa sai ta tsame kanta daga shari’ar.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp