fidelitybank

Kotu ta cigaba da tsare wanda ya bayyana cewa Tinubu zai gayyato Sojojin Faransa

Date:

Kotun Majistare da ke Kaduna ta bayar da umarnin tsare Mahadi Shehu, fitaccen mai sharhi daga Kaduna, har zuwa ranar 14 ga Janairu, 2025, domin ci gaba da sauraron ƙarar da ake masa.

Shehu na fuskantar tuhuma guda biyu, ciki har da haɗin baki da taimakawa ayyukan ta’addanci, wanda ya saba wa sashe na 26 (2)(3) na Dokar Hana Ta’addanci ta 2022, da kuma tada hankalin jama’a, wanda ya saba wa sashe na 78 na Dokar Penal Code ta jihar Kaduna ta 2017.

Alƙalin kotun, Abubakar Lamiɗo, ya bayar da umarnin tsare Shehu a gidan gyaran hali na Kaduna bayan da aka gurfanar da shi gaban kotu a ranar Talata.

Wannan tsarewar na zuwa ne bayan zarginsa da wallafa wani saƙon da ya nuna cewa gwamnatin tarayya na shirin kafa sansanin sojojin Faransa a Arewa maso Gabas, wanda gwamnatin Najeriya ta musanta.

Bincike daga kafafen yada labarai ya tabbatar da cewa bidiyon da aka yi amfani da shi wajen yada wannan zargi ba gaskiya ba ne, yana dauke da sojojin Najeriya a Arewacin Mali, kuma an fara wallafa shi a YouTube tun a watan Janairu na 2013.

Mahadi Shehu ya kasance a hannun hukumar tsaron farin kaya (DSS) kafin gurfanar da shi gaban kotu.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp