fidelitybank

Kotu ta cigaba da tsare wanda ya bayyana cewa Tinubu zai gayyato Sojojin Faransa

Date:

Kotun Majistare da ke Kaduna ta bayar da umarnin tsare Mahadi Shehu, fitaccen mai sharhi daga Kaduna, har zuwa ranar 14 ga Janairu, 2025, domin ci gaba da sauraron ƙarar da ake masa.

Shehu na fuskantar tuhuma guda biyu, ciki har da haɗin baki da taimakawa ayyukan ta’addanci, wanda ya saba wa sashe na 26 (2)(3) na Dokar Hana Ta’addanci ta 2022, da kuma tada hankalin jama’a, wanda ya saba wa sashe na 78 na Dokar Penal Code ta jihar Kaduna ta 2017.

Alƙalin kotun, Abubakar Lamiɗo, ya bayar da umarnin tsare Shehu a gidan gyaran hali na Kaduna bayan da aka gurfanar da shi gaban kotu a ranar Talata.

Wannan tsarewar na zuwa ne bayan zarginsa da wallafa wani saƙon da ya nuna cewa gwamnatin tarayya na shirin kafa sansanin sojojin Faransa a Arewa maso Gabas, wanda gwamnatin Najeriya ta musanta.

Bincike daga kafafen yada labarai ya tabbatar da cewa bidiyon da aka yi amfani da shi wajen yada wannan zargi ba gaskiya ba ne, yana dauke da sojojin Najeriya a Arewacin Mali, kuma an fara wallafa shi a YouTube tun a watan Janairu na 2013.

Mahadi Shehu ya kasance a hannun hukumar tsaron farin kaya (DSS) kafin gurfanar da shi gaban kotu.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp