fidelitybank

Kotu ta ce a yi wa Hafsat Chuchu gwajin ƙwaƙwalwa bayan ta kashe mijinta

Date:

Wata babbar kotu da ke zaman ta a birnin Kano ta buƙaci a yi wa Hafsat Surajo (Chuchu) gwajin taɓin hankali a ci gaba da shari’ar da ake yi mata kan zargin kisan wani matashi mai suna Nafi’u Hafiz.

Kotu ta ɗauki wannan mataki ne bayan da Hafsat ta ƙi cewa uffan a lokacin da aka karanta mata tuhumar da ake yi mata.

Kotun ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Zuwaira Yusuf ta buƙaci a samu likitan ƙwaƙwalwa da zai duba lafiyar Hafsat a inda ake tsare da ita.

Tun farko an karanta wa Hafsat laifukan da ake tuhumar ta da su, sai dai ba ta ce komai ba a lokacin da kotu ta tambaye ta ko ta fahimci abin da ake nufi ko a’a, balle ma ta amsa ko tana da hannu a cikin abin da ake zargin nata da shi ko a’a.

Yanzu haka kotun za ta jira sakamakon gwajin da likita zai yi wa Hafsat kafin ci gaba da sauraron shari’ar.

A cewar kotu, dole ne a tantance lafiyar duk wanda ake tuhuma kafin ci gaba da shari’a, kasancewar “ba a yin shari’a da mai taɓin hankali.”

Wannan ne karo na farko da ake karanto wa Hafsat tuhume-tuhumen da ake yi mata a gaban babbar kotun.

An gabatar da ita ne a kotun tare da mijinta da kuma wasu mutum biyu da ake zargi da hannu wajen aikata laifin.

Haka nan a lokacin zaman na yau Alhamis, lauyoyin waɗanda ake tuhuma sun gabatar wa kotu buƙatar bayar da belin mjin na Hafsat da sauran mutum biyun, sai dai kotun ta ce za ta sanya ranar sauraron buƙatar tasu.

A watan Disamban shekarar da ta gabata ne rundunar ƴansanda a jihar Kano ta bayyana cewa jami’anta sun kama Hafsat Surajo ƴar shekara 24 da ke Unguwa Uku bisa zargin kashe Nafi’u Hafiz, ɗan shekara 38 a gidanta na aure.

Haka zalika binciken ƴansandan ya kai ga kama mijin matashiyar, Dayyabu Abdullahi mai shekara 38, sai kuma Mallam Adamu mai shekara 65 da kuma ƙarin wani mutum ɗaya.

Tun a wancan lokaci ne kotu ta bayar da umarnin ajiye Hafsat a gidan kaso.

Bayan kammala zaman kotun na yau an mayar da Hafsat da sauran waɗanda ake tuhuma zuwa gidan gyaran hali domin ci gaba da tsare su.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp