A ranar Litinin ɗin nan ne wata babbar kotun shari’ar musulunci da ke Kano ta yanke wa Shafi’u Abubakar, matashin nan da aka tuhuma da ƙona masallata hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan samun shi da aikata laifin kisan kai.
Al’amarin da ya faru ne a gari Gadan da ke ƙarƙashin Larabar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a jihar Kano.
A ranar 15 ga watan Mayun 2024 ne matashin ya zuba fetur sannan ya cinna wa mutanen wuta yayin da suke yin sallar Asuba, lamarin da ya janyo da dama daga cikinsu suka kone sannan wasu suka mutu.
An ruwaito cewa lamarin ya faru ne sanadiyyar rikici kan rabon gado tsakaninsa da ƴan uwansa.