fidelitybank

Kotu ta ce a kwace dala 899,900 daga wajen Ahmed Idris

Date:

Wata babbar kotu ta bayar da umarnin kwace dala 899, 900 da naira miliyan 304, 490, 160. 95 da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta karbo daga hannun tsohon Akanta Janar din Najeirya Ahmed Idris.

Mai shari’a M. A Haasan ne ya bayar da umarnin a zaman kotun a ranar 13 ga Disambar da muke ciki, yayin da yake yanke hukunci kan ƙarar da hukumar EFCC a Najeriya ta shigar gabanta.

Haka kuma kotun ta umarci da a karbe kadarori 15 mallakinsa da ke Kano da Abuja.

Kadarorin da aka bayar da umarnin a kwace sun haɗa da babban kantin sayar da kaya na Al-Iklas, da wasu shaguna a Ladanai, da gidan gidan alfarma na unguwar Daneji dukkan su da ke Kano.

Haka sai gidansa da ke Karsana a Abuja, da wani plotin, dake rukunin gidaje na Blue Fauntain shima a baban birnin Najeriyar Abuja.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Ahmed Idris da ƙarin wasu mutane, gaban kotun ne kan zargin aikata wasu laifuka 14 da ke da alaƙa da sata da halarat kuɗin haram da kiyasin su ya kai naira bilyan109.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp