Kotu ta soke belin da ta baiwa tsohon kwamishinan ayyuka na Jihar Kano, Mu’azu Magaji Dan Sarauniya.
An soke belin ne saboda rashin bayyanarsa a gaban kotu har sau uku, domin amsa tuhumar da ake masa na bata sunan Gwamna Abdullahi Ganduje.
Kotun ta kuma yi umurnin a kama Dan Sarauniya tare da mika sammaci ga mutane biyun da suka tsaya masa.
Babbar kotun majistare ta soke belin ne a ranar ranar 4 ga watan Fabrairu, kuma cikin mutanen da su ka tsaya masa su ma dole su mika kansu ga kotun, domin amsa tambayoyi.