Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai shari’a Halima Nasir ta yanke wa wani matashi mai suna Anas Umar hukuncin kisan kai ta hanyar rataya, bisa laifin kashe wani Ashiru a karamar hukumar Tudun Wada.
An zargi Anas Umar da gayyatar Ashiru zuwa wata gona da ake kira Sambisa a garin Tudunwada, inda ya buga masa gora abin da ya yi ajalinsa.
Lauyan gwamnatin jihar Kano, Barista Ibrahim Arif Garba, ya gabatar da shaidu a gaban kotu, wanda suka gamsar da mai shari’a.
Kotun ta yi watsi da shaidun da lauyan kariya, Barista Shehu Sani, ya gabatar.
A karshe, mai shari’a Halima Nasir ta yanke wa Anas Umar hukuncin kisa ta hanyar rataya.