Babbar Kotun Jihar Ribas ta yanke wa wani mutum mai suna Bestman Lekia hukuncin kisa ta hanyar rataya, bisa laifin kashe mutane hudu tare da yin amfani da guda daya daga cikin hanjin da ya kashe wajen shirya a unguwar Okwalie da ke karamar hukumar Khana a Jihar Ribas.
Kotun ta kuma samu Lekia da laifin fashi da makami, garkuwa da mutane, kungiyar asiri da kuma sata.
An bayyana cewa wanda aka yankewa hukuncin da ‘yan kungiyar sa, sun kashe Nenalebarri Mmeabe, Loveday Mmeabe, Gbodu Nobale da Etim Ekpe.
Lekia da ‘yan kungiyarsa sun fara yin garkuwa da Loveday Mmeabe a shekarar 2019, suka cire masa hanjinsa kuma suka yi amfani da su wajen shirya abincin miya.
Mai shari’a Adolphus Enebeli ya ce lauyan da ya shigar da kara ya tabbatar da hujjar sa fiye da kowane kwakkwarar hujja inda ya ce a rataye Lekia a wuyansa har sai an tabbatar da mutuwarsa.
Mai shari’a Enebeli ya lura cewa halin Lekia a duk lokacin shari’ar da ake yi masa ya tabbatar da cewa shi mutum ne mai taurin kai, dan ta’adda da kungiyar asiri.
Da yake mayar da martani kan hukuncin, mai shigar da kara na jihar, Chidi Ekeh, ya bayyana hukuncin a matsayin haziki, yana mai cewa zai ceto al’ummar Ogoni da jihar Rivers.
Da yake karin haske, Ekeh ya ce a matsayinsa na dan Adam bai ji dadin yadda aka yanke wa wani hukuncin kisa ba, amma da a ce jihar ta gaza a cikin al’umma idan da a ce an bar Lekia ta rika tafiya ba tare da fuskantar shari’a ba.