fidelitybank

Kotu ta bayar da izini a kashe ‘yan Bijilante 5 a Kano

Date:

Wata babbar kotu a jihar Kano ta yanke wa wasu `yan banga biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan ta kama su da laifin kisan wani matashi mai shekara 17.

‘Yan bangar sun aikata laifin ne a ranar 22 ga watan Janairun 2022.

‘Yan bangar, waɗanda suke aiki a cibiyar bunƙasa rayuwar matasa ta Sani Abacha da ke kan hanyar Madobi, sun haɗa da Emmanuel Korau da Elisha Ayuba da Irimiya Timothy da Auwalu Jafar da kuma Mustapha Haladu.

Lauyan da ya gabatar da kara Barrister Lamido Soron Dinki, gabannin yanke hukuncin ya shaida wa kotun cewa waɗanda ake zargi sun kama matashin ne a sabon titi, Panshekara, inda suka far masa da duka da da sanduna, kana daga bisani suka raunata shi ta hanyar caka masa wuka, kana suka ja shi a kasa suka jefa shi cikin keken a daidaita sahu, lamarin da ya yai sanadin mutuwarsa.

Lauyan waɗanda aka yi ƙarar ya yi ƙokarin kare su, inda ya bayyana cewa sun je ne da nufin kama matashin ba halaka shi ba, bayan an kai musu karan sa.

Sai dai, kamar yadda mai magana da yawun kotunan jihar Kano, Malam Baba Jibo Ibrahim ya ce, mai shara`a Dije Aboki ta yanke wa `yan bangan hukunci ne bayan ta gamsu da hujjojin da mai gabatar da ƙarar ya gabatar:

Sai dai kuma mutanen da aka yanke wa hukuncin na da damar ɗaukaka ƙara.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp