fidelitybank

Kotu ta bayar da belin tsohon gwamnan Kwara kan kudi miliyan 50

Date:

Babbar kotun tarayya da ke brnin Ilorin a jihar Kwara ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar, Abdulfattah Ahmed kan kudi naira miliyan 50 tare da sharadin mutum biyu da za su tsaya masa wadanda suka mallaki fili a birnin Ilorin.

Haka kuma cikin sharadin belin tsohon gwamnan zai ajiye fasfo dinsa na tafiye-tafiye da sauran sharuda.

Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ta gurfanar da tsohon gwamnan ne a ranar Juma’a, biyo bayan gayyatar da hukumar ta yi masa domin amsa tambayoyi a ranar Litinin.

Sai dai kuma an hana ‘yan jarida shiga kotun.

Hukumar EFCC ta kama Ahmed a ranar Litinin inda ake yi masa tambayoyi kan hada-hadar biliyoyin naira a lokacin da yake gwamnan jihar.

Ahmed ya kasance gwamnan jihar Kwara tsakanin watan Mayun 2011 zuwa Mayu 2019 kafin ya mikawa Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq.

An taba yi masa tambayoyi a watan Mayun 2021 a hedikwatar EFCC da ke unguwar Jabi a Abuja, babban birnin kasar, kan zargin karkatar da kuÉ—ade kusan Naira biliyan 9 daga asusun jihar.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp