fidelitybank

Kotu ta bayar da belin mutumin da ya gartsa wa Dan Sanda cizo

Date:

Wata Kotun Majistare da ke Ejigbo a Jihar Legas, a ranar Alhamis, ta bayar da belin wani Tijani Muiz a kan kudi Naira 400,000, wanda ake zargi da cizon dan sanda da ke bakin aiki.

Alkalin kotun, A. K. Dosunmu, ta kuma umurci wanda ake kara ya gabatar da masu tsaya masa guda biyu a daidai wannan adadi.

Ta ba da umarnin cewa dole ne a yi amfani da wadanda za su tsaya wa aiki tare da nuna shaidar biyan haraji ga gwamnatin jihar Legas.

Ta dage sauraron karar har zuwa ranar 23 ga watan Agusta. Muiz, wanda ba a bayar da adireshinsa ba, yana fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume guda uku na kai hari, da aikata laifin da zai iya haifar da rashin zaman lafiya da kuma cikas ba bisa ka’ida ba.

Sai dai ya musanta zargin da ake masa. Dan sanda mai shigar da kara, Insp Benedict Aigbokhan, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne a ranar 24 ga watan Yuli da karfe 9.30 na dare. a kofar Jakande, Ejigbo, jihar Legas.

A cewar Aigbokhan, wanda ake tuhuma ya hana Insp Raymond Maugbe gudanar da aikinsa na hukuma.

“A yayin da yake hana jami’in gudanar da aikinsa na hukuma, wanda ake tuhuma ya ci zarafin jami’in ta hanyar cizon sa a yatsansa na hagu,” in ji shi.

Aigbokhan ya kara da cewa wanda ake tuhuma ya gudanar da kansa ta hanyar da za ta iya kawo cikas ga zaman lafiyar jama’a.

Ya ce, laifukan sun ci karo da sashe na 168 (d), 173 da 174 (b) na dokar laifuka ta jihar Legas, 2015.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp