fidelitybank

Kotu ta bayar da belin Emefiele daga hannun EFCC

Date:

Mai sharia’a Olukayode Adeniyi na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bayar da belin tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele.

Alƙalin ya bayar da umarnin sakin Emefiele nan take ga lauyoyinsa, waɗanda aka ɗora wa alhakin kai shi kotu a zaman da za a yi a makon gobe da kuma duk lokacin da ake buƙata.

Alƙalin ya kuma ce wajibi ne ga tsohon shugaban bankin na CBN ya ajiye dukkanin takardun tafiye-tafiyensa a hannun magatakardar kotun kafin shari’ar ta kankama.

Haka nan ta kuma ce dole ne a daina tsare shi ba tare da shari’a ba.

Kotun ta ce ba za ta kawar da idonta daga batun cewa ya shafe kwana 151 a tsare ba, kuma kotun ta ce dole ne gwamnatin tarayya da ministan shari’a su martaba umarnin kotu.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp