fidelitybank

Kotu ta baiwa Rochas izini zuwa Burtaniya samun lafiya

Date:

A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta baiwa tsohon gwamnan jihar Imo, Anayo Rochas Okorocha, izinin tafiya kasar Burtaniya domin neman lafiya.

Mai shari’a Inyang Eden Ekwo, wanda ya ba da izinin, ya umarci magatakardar kotun da ya ba shi fasfo din tafiya na tsohon gwamnan domin gudanar da ziyarar jinya.

Umurnin alkalin ya biyo bayan bukatar da wani babban Lauyan Najeriya, Mista Ola Olanipekun ya yi, wanda ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa na fama da matsalar lafiya a ‘yan kwanakin nan.

Babban Lauyan ya bayyana cewa, Okorocha, wanda yanzu Sanata ne mai wakiltar Imo ta Arewa a Majalisar Dattawa, ba zai yi amfani da wannan umarni ba, kuma zai dawo kasar domin yi masa shari’a.

Ko da yake, Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, wanda Mista Chile Okoroma ya wakilta ya nemi yin kakkausar suka da wannan bukata, hukumar ta tausasa murya lokacin da Mai Shari’a Ekwo ya bayyana cewa za a amince da bukatar tare da gargadin kotu.

Yayin da yake amsa wannan bukata, Mai shari’a Ekwo ya umarci Okorocha da ya mayarwa magatakardar kotun fasfo din kasa da kwanaki uku da isowarsa kasar.

Alkalin kotun ya ce zai bayyana Okorocha na nemansa idan ya yi yunkurin yin amfani da damar da aka yi masa.

Daga nan ne mai shari’a Ekwo ya sanya ranar 7 ga watan Nuwamba domin ci gaba da shari’ar sa kan tuhume-tuhumen da gwamnatin tarayya ta gabatar masa.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp