fidelitybank

Kotu ta baiwa Rochas izini zuwa Burtaniya samun lafiya

Date:

A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta baiwa tsohon gwamnan jihar Imo, Anayo Rochas Okorocha, izinin tafiya kasar Burtaniya domin neman lafiya.

Mai shari’a Inyang Eden Ekwo, wanda ya ba da izinin, ya umarci magatakardar kotun da ya ba shi fasfo din tafiya na tsohon gwamnan domin gudanar da ziyarar jinya.

Umurnin alkalin ya biyo bayan bukatar da wani babban Lauyan Najeriya, Mista Ola Olanipekun ya yi, wanda ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa na fama da matsalar lafiya a ‘yan kwanakin nan.

Babban Lauyan ya bayyana cewa, Okorocha, wanda yanzu Sanata ne mai wakiltar Imo ta Arewa a Majalisar Dattawa, ba zai yi amfani da wannan umarni ba, kuma zai dawo kasar domin yi masa shari’a.

Ko da yake, Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, wanda Mista Chile Okoroma ya wakilta ya nemi yin kakkausar suka da wannan bukata, hukumar ta tausasa murya lokacin da Mai Shari’a Ekwo ya bayyana cewa za a amince da bukatar tare da gargadin kotu.

Yayin da yake amsa wannan bukata, Mai shari’a Ekwo ya umarci Okorocha da ya mayarwa magatakardar kotun fasfo din kasa da kwanaki uku da isowarsa kasar.

Alkalin kotun ya ce zai bayyana Okorocha na nemansa idan ya yi yunkurin yin amfani da damar da aka yi masa.

Daga nan ne mai shari’a Ekwo ya sanya ranar 7 ga watan Nuwamba domin ci gaba da shari’ar sa kan tuhume-tuhumen da gwamnatin tarayya ta gabatar masa.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp