fidelitybank

Kotu ta baiwa PDP da NNPP damar duba kayan zaɓen INEC a Bauchi

Date:

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Bauchi da ta ‘yan majalisar dokokin jihar da ta kasa, ta ba dan takarar jam’iyyar PDP, Garba Dahiru izinin samun wasu muhimman kayayyakin da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta yi amfani da su a zaben da a ka yi a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Mai shari’a Wilfred Kpochi, wanda ya jagoranci kwamitin mutum uku, ya ba da wannan umarni ne biyo bayan takardar karar da Dahiru da jam’iyyarsa suka shigar.

INEC ta sanar da Shehu Umar na APC a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar Bauchi ta Kudu a ranar 26 ga watan Fabrairu.

Karanta Wannan: Shugaban INEC ka yi murabus kawai – Melaye

Shugaban Lauyan mai shigar da kara, Alex Hassan, ya roki kotun da ta tilasta wa INEC ta baiwa wanda yake karewa damar samun takardu a hannun hukumar da aka yi amfani da su wajen gudanar da zaben, inda ya kara da cewa takardar za ta taimaka masa wajen kalubalantar fitowar Umar na APC a matsayin wanda ya lashe zaben. zaben.

Mai shari’a, Kpochi wanda ya ba da bukatar kuma ya ce yana da cancanta.

Don haka ya umurci INEC da ta samar da kayan zaben ga mai bukata da wakilansa da kuma lauyoyinsa.

“Masu shigar da kara za su dauki kwafi da aka tabbatar da su sannan su gudanar da aikin tantance kayan zabe da aka yi amfani da su wajen gudanar da zaben Sanatan Bauchi ta Kudu da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023,” in ji shi.

Kotun ta kuma ba wa dan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Mijinyawa Mohammed izinin samun kayan zaben da aka yi amfani da shi wajen zaben Sanatan Bauchi ta Arewa.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp