fidelitybank

Kotu ta baiwa gwamnoni kwana 7 su kare kansu a kan kananan hukumomi

Date:

Kotun ƙoli ta umarci gwamnonin jihohin kasar nan 36, da su kare kansu cikin kwanaki bakwai, kan ƙarar da gwamnatin tarayya ta shigar na neman cikkaken ‘yancin gashin kai ga ƙananan hukumomi 774.

A zaman kotun na yau alakalai bakwai ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Garba Lawal, kotun ta bai wa gwamnonin jihohi 36 umurnin shigar da bayanan kare kansu a gabanta a cikin kwanaki bakwai daga yau.

Alƙalan sun bai wa babban lauya, Lateef Fagbemi umurnin bayyana martaninsa da ke nuna matsayar gwamanati a cikin kwana biyu da shigar da nasu ƙorafin kariya.

A karar da gwamnatin tarayyar ta shigar ta hannun babban lauyanta Lateef Fagbemi ya kuma nemi kotun ta bayar da damar da za a iya tura wa ƙananan hukumomin kuɗaɗensu daga asusun gwamnatin tarayya kai tsaye, kamar yadda ƙundin tsarin mulkin kasa ya bayar.

Babban lauyan ya kuma ce yin wani abu saɓanin hakan daidai ya ke da karya dokokin ƙasa da ƙundin tsarin mulkin shekarar 1999 ya bayar da dama.

Gwamnatin tarayyar ta kuma roƙi kotun ƙolin ta yi la’akari da sashe na ɗaya da na huɗu da na biyar waɗanda suka tilasta wa gwamnonin da ‘yan majalisar dokokin jihohi su tabbatar da cikakken tsarin dimokradiyya a mataki na ƙasa ba wai kama karya ba irin yadda ake yi a yanzu.

Kotun ƙolin ta ce dole ne a kammala gabatar da dukkan matakai da musayar bayanai da suka kamata a kan lokaci, inda ta sanya ranar 13 ga watan Yuni don sauraron bayanan ƙarar da gwamnonin za su shigar.

Gwamnonin jihohin na ci gaba da iko da kusan komai na ƙananan hukumomi 774 a kasar nan.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp