fidelitybank

Kotu ta baiwa Gwamnati dama ta tuhumi Matawalle kan zargin tallafawa ƴan bindiga a Zamfara

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince da karar da ke neman tilasta wa Gwamnatin Tarayya ta binciki zargin alakanta Karamin Ministan Tsaro, Alhaji Bello Matawalle da zargin tallafawa ‘yan bindiga a Jihar Zamfara.

Karamin wanda dan rajin kare hakkin bil’adama, Abubakar Dahiru ya kawo, na da nufin gudanar da bincike kan zargin da Matawalle ya yi na hannu a ayyukan ‘yan bindiga a lokacin da yake gwamna.

Takardar karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1434/2024, ta bayyana shugaban kasa Bola Tinubu, da babban lauyan gwamnatin tarayya, da Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP) a matsayin wadanda ake kara na 1, 2, da na 3, bi da bi.

Dahiru, wanda lauyansa Ojonimi Apeh ya wakilta, yana rokon kotun da ta bayyana cewa dole ne shugaba Tinubu ya umurci IGP ya binciki ayyukan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara, tare da mayar da hankali musamman kan zarge-zargen da Matawalle ke takawa a rikicin.

Mai shigar da karar ya ce a lokacin Matawalle yana gwamna (2019-2023), ‘yan fashi da makami sun ta’azzara zuwa matakin da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ya sa dubban al’ummar jihar Zamfara suka rasa matsugunansu, ko marayu, ko kuma zawarawa saboda tashin hankalin.

Dahiru ya yi nuni da hirarraki da kasidu da ke zargin Matawalle da goyon bayan ‘yan fashi, ciki har da ikirarin cewa ya bai wa ‘yan bindigar motoci, da yin zagon kasa ga kokarin tabbatar da doka da oda, da yin afuwa ga ‘yan ta’adda.

Dahiru ya kara da cewa, duk da wadannan munanan zarge-zarge, gwamnati ba ta yi wani yunkuri na binciken Matawalle ba, yayin da ‘yan fashi ke ci gaba da addabar jihar Zamfara. In ji Daily Post.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp