fidelitybank

Kotu ta baiwa EFCC dama ta tuhumi Yahaya Bello ta hannun lauyansa

Date:

Mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya bayar da umarnin a gurfanar da tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Adoza Bello, kan zargin almundahanar Naira biliyan 80 da gwamnatin tarayya ta shigar ta hannun lauyansa, Abdulwahab Mohammed.

Alkalin ya bayar da wannan umarni ne a ranar Talata yayin da yake yanke hukunci a cikin takardar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC ta shigar na neman maye gurbin Bello.

Babbar Lauyan Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Kemi Pinheiro, Babbar Lauyan Najeriya, ta yi muhawara kan bukatar.

Duk da cewa da farko lauyan Bello Abdulwahab Mohammed ya ki amincewa da tuhume-tuhumen da hujjojin shaidu, amma mai shari’a Nwite ne ya tilasta masa yin hakan.

Alkalin kotun ya ki amincewa da rokon da babban lauyan ya yi na cewa karamin lauya a tawagar sa, AI Musa shi ne zai karbi tuhumar a madadin tsohon gwamnan.

A zaman da aka yi a ranar Talata, Yahaya Bello bai sake zuwa kotu ba amma lauyansa ya wakilce shi.

A makon jiya ne mai shari’a Nwite ya bayar da sammacin benci a kan Bello sakamakon bukatar da EFCC ta yi masa.

Daga nan ne hukumar EFCC ta bayyana cewa ana neman tsohon gwamnan ne saboda dagewar da ya yi a gaban kotu da kuma kaucewa tuhumar da ake masa.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp