fidelitybank

Kotu ta baiwa Atiku da Obi damar duba kayan zabe

Date:

Kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ta bai wa ɗan takarar shugaban kasa a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na Labour, Peter Obi damar duba kayayyakin da aka yi amfani da su a zaɓen ranar 25 ga watan Fabarairu.

Tun farko ƴan takarar ne daban-daban suka miƙa buƙatar neman a ba su damar duba kayayyakin da aka yi amfani da su a babban zaɓen 2023 tare da tilasta wa INEC ta ba su damar ganin kayan aikin da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasar.

A ranar Laraba 1 ga watan Maris ne Atiku Abubakar ya shigar da tasa ƙarar yayin da Peter Obi kuma ya shigar da tasa ranar Alhamis biyu ga watan.

Kan haka ne kotun ta umarci hukumar zaɓe ta bai wa ɗan takarar PDP damar duba kayayyakin zaɓen.

A yau Juma’a kuma kotun ta amsa bukatun ‘yan takarar na duba kayan zaɓen sannan kuma su titsiye hukumar zaɓe kan wasu bayanai da za su buƙata.

Kotun ƙarƙashin mai shari’a Joseph Ikyegh ta bayar da umarnin ne bayan da ta saurari wasu ƙararraki da ƴan takarar biyu suka shigar tare da jam’iyyunsu.

PDP da LP waɗanda a baya-bayan nan suka yi watsi da sakamakon zaɓen, sun ce samun damar ganin kayayyakin za ta taimaka musu a ƙalubalantar sakamakon zaɓen da suke yi wanda ya ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara.

A cewar INEC, Tinubu ya ci zaɓen ne da ƙuri’u 8,794,726 inda Atiku Abubakar na PDP yake bi masa da ƙuri’u 6,984,520 sai Obi na Labour Party da ya zo na uku da ƙuri’u 6,101,533.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...
X whatsapp