Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano, ta ajiye hukunci a karar da jam’iyyar APC ta shigar na kalubalantar nasarar gwamna Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP.
Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay, shugaban kwamitin mutane uku, wanda ya yi alkawari a madadin kwamitin na yin adalci ga dukkan bangarorin, ya ce hukuncin zai zo ne kafin kwanaki 180 da doka ta ba su.
Dage zaman ya biyo bayan jawaban karshe da bangarorin biyu suka yi.
Yayin da ta ke gabatar da jawabi na karshe ga kotun, APC ta bukaci kotun da ta tabbatar da karar da ta shigar ta kuma mayar da Nasir Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.
Yayin da INEC, NNPP da Yusuf suka bukaci kotun ta yi watsi da karar.
A halin da ake ciki rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta haramta zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da magoya bayansu ke yi.
Kwamishinan ‘yan sanda, Usaini Gumel, ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Kano yayin da yake ganawa da manema labarai a hedikwatar rundunar a ranar Litinin da ta gabata a Kano.