fidelitybank

Kotu ta ajiye hukunci na ayyana sakamakon karshe a zaben gwamnan Kano

Date:

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano, ta ajiye hukunci a karar da jam’iyyar APC ta shigar na kalubalantar nasarar gwamna Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP.

Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay, shugaban kwamitin mutane uku, wanda ya yi alkawari a madadin kwamitin na yin adalci ga dukkan bangarorin, ya ce hukuncin zai zo ne kafin kwanaki 180 da doka ta ba su.

Dage zaman ya biyo bayan jawaban karshe da bangarorin biyu suka yi.

Yayin da ta ke gabatar da jawabi na karshe ga kotun, APC ta bukaci kotun da ta tabbatar da karar da ta shigar ta kuma mayar da Nasir Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

Yayin da INEC, NNPP da Yusuf suka bukaci kotun ta yi watsi da karar.

A halin da ake ciki rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta haramta zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da magoya bayansu ke yi.

Kwamishinan ‘yan sanda, Usaini Gumel, ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Kano yayin da yake ganawa da manema labarai a hedikwatar rundunar a ranar Litinin da ta gabata a Kano.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp