fidelitybank

Kotu ta aike da Manomi zuwa gidan gyaran hali da tuhumar kisan kai

Date:

Babban Kotun Majistare da ke Makurdi a jihar Benue, a ranar Juma’a ta bayar da umarnin tsare wani manomi mai shekaru 50, Aka Anyam, a gidan gyaran hali, bisa zarginsa da kashe wani Gabriel Ayia.

Mista Annyam, wanda dan asalin garin Tse-Norum ne, a karamar hukumar Gwer-East ta jihar Benue, an tuhume shi da laifin hada baki, wanda ya haddasa mummunan rauni da kuma kisa.

Lauyan masu shigar da kara, Godwin Ato, ya shaida wa kotun cewa an kai karar ga kwamishinan ‘yan sandan Benue ta wata kara a ranar 22 ga watan Afrilu.

Mista Ato ya ce, Bello Weren Esq ne ya rubuta koken a madadin wanda ya kai karar, Godwin Ayia, da ke zaune daura da gidan Rediyon Benue, Makurdi, kan iyalan Awolowo Norum na Tse-Norum, karamar hukumar Gwer-West ta jihar Benue.

Mai shigar da karar ya yi zargin cewa, wani lokaci a shekarar 2014, danginsa sun samu sabani da dangin Awolowo Norum.

Ya ce, daga nan ne aka kai rahoton lamarin ga sarakunan gargajiyar kasar, kuma suna ta bincike har zuwa yau. In ji People Gazzete.

Sai dai ya ce, bayan wani lokaci sai ‘yan uwan ​​Awolowo suka shiga tashin hankali suka fara kai wa ‘yan uwansa hari.

Mai shigar da karar ya ce ba shi da wani zabi illa ya kai rahoton lamarin a hedikwatar ’yan sandan yankin da ke Makurdi a ranar 11 ga watan Maris kuma an aike da ‘yan sanda hudu tare da shi domin kamo maharan.

Ya  kuma ce, a lokacin da ya isa Tse-Norum, ’yan gidan Awolowo 16 ne suka kai masa hari tare da ‘yan sanda tare da yi masa rauni a ka.

Mai shigar da karar ya ci gaba da cewa, a ranar 13 ga Afrilu, wadannan mutane sun kai wa dan uwansa, Jibrilu hari a gonarsa, inda suka yi masa duka tare da yi masa yanka har lahira.

Mai gabatar da kara ya kara da cewa tun da farko an kama mutane biyar aka gurfanar da su a gaban kuliya yayin da wanda ake zargin wanda ke boye a lokacin an kama shi. Sai dai Mista Ato ya ce har yanzu akwai sauran da dama.

Lauyan mai gabatar da kara ya ce laifukan sun ci karo da tanadin sashe na 97, 248 da 222 na dokokin Penal Code na Benue, 2004.

Babban Alkalin Kotun, Vincent Kor, bai dauki karar wanda ake zargin ba na neman hurumin hukumta, kuma ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 29 ga watan Agusta, domin karin bayani.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp