Wata babbar kotu da ke Kano a Najeriya ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan kama su da laifin kisan wata tsohuwa bisa zargin maita.
Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin yin silar mutuwar tsohuwar mai shekara 67 a duniya a ranar 15 ga watan Nuwamban 2023, ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba.
A lokacin yanke hukuncin, mai shari’a Usman Na’abba ya bayyana cewa kotun ta samu hujjoji Æ™arara da suka tabbatar da laifin waÉ—anda ake tuhuma.
Lamarin dai ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke ƙaramar hukumar Wudil ta jihar Kano.
Maita da tsafi abubuwa ne da ke yawan janyo cece-ku-ce a ƙasashen Afirka, inda iyalai kan ɗauki mataki kan mutanen da suke zargi da kashe musamman yara ta hanyar maita.