fidelitybank

Kotu ta ɗage shari’ar Binance da EFCC

Date:

Babbar kotun birnin Tarayya, ta ɗage sauraron ƙarar halasta kuɗin haram da aka shigar kan ma’aikatan kamfanin hada-hadar kuɗin kirifto na Binance zuwa ranar 17 ga watan Mayu.
An sanya ranar zaman shari’ar yau Alhamis sai dai a yanzu, an sake dage shari’ar.
Hukumar EFCC ce ta gurfanar da Binance da ma’aikatanta biyu, Tigran Gambarayan da Nadeem Anjarwalla da laifin halasta kuɗin haram da ya kai dala miliyan 35.4.
Lauyan Gambarayan ya shaida wa kotu cewa, ba a bai wa wanda yake karewa takardun kotu ba, domin haka ya roƙi kotu ta jinkirta ƙarar.
Ita ma hukumar tattara haraji ta kasa na tuhumar Binance da ma’aikatan na ta da laifuka biyar da suka shafi kauce wa biyan haraji.
Tigran Gambarayan, wanda ɗan Amurka ne, ya musanta zargin tuhume-tuhumen da ake yi masa, yayin da har yanzu ake neman abokin aikinsa Nadeem Anjarwalla ruwa a jallo, bayan ya tsere daga gidan gyaran hali a watan Maris.
Gambarayan, mai shekara 39 zai ci gaba da zama a tsare, har sai ranar 17 ga watan Mayu da za a ci gaba da zaman shari’ar.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp