fidelitybank

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Date:

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar da hukuncin kotun tarayya na cewa fiye da motoci 40 da aka kwato daga gidan tsohon Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, mallakin gwamnatin jiha ne.

Alƙalai uku ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a A.M. Talba sun yi watsi da ƙarar da Matawalle ya shigar, inda suka bayyana cewa bai gabatar da kwararan hujjoji da ke tabbatar da cewa shine mai mallakar motocin ba.

Lamarin ya samo asali ne tun watan Yuni a shekarar 2023, lokacin da gwamnatin Zamfara ta bai wa tsohon gwamnan da mataimakinsa kwanaki biyar su dawo da motocin gwamnati da suka kwashe bayan sauka daga mulki, amma suka ƙi. Daga bisani kotu ta bayar da izinin jami’an ‘yan sanda su kwato su.

Kakakin gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya ce wannan hukunci ya tabbatar da cewa motocin za su ci gaba da kasancewa mallakin gwamnatin Zamfara, tare da bai wa ‘yan sanda damar cigaba da bincike da kuma yiwuwar gurfanar da masu laifi.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...
X whatsapp