fidelitybank

Kotu na neman ‘yar kasuwa ruwa a jallo

Date:

Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Ikeja ta soke belin wata ‘yar kasuwa mai suna Blessing Adanu.

An dai gurfanar da Adanu ne bisa zargin damfarar wanda take karewa Naira miliyan 47.

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ce ta gurfanar da wanda ake tuhumar.

Tana fuskantar tuhume-tuhume biyu na samun kudi ta hanyar karya da kuma sata.

Wadda ake zargin ta ki amsa laifin da ake tuhumarta da shi a lokacin da aka gurfanar da ita a ranar 19 ga watan Disamba, 2019.

A yau ne mai shari’a Mojisola Dada ta janye belin ta tare da umurci hukumar EFCC da ta bayyana wanda ake nema ruwa a jallo.

Alkalin kotun ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 2 ga watan Disamba domin amincewa da rubutaccen adireshin karshe.

Lauyan EFCC, Samuel Daji ya ce shari’ar da aka shirya na karbar adireshin karshe ba za ta iya ci gaba ba saboda rashin halartar Adanu.

Don haka lauyan hukumar ya mika takardar bukatar kotun da ta janye belin.

Lauyan da ake kara, Olarenwaju Ajanaku bai yi adawa da bukatar masu gabatar da kara ba.

Ajanaku ya shaida wa alkalin cewa shi ma ya yi mamakin yadda wanda yake karewa bai zo kotu ba.

Ana tuhumar Adanu ne da yin kasuwanci a karkashin Emerald Multipurpose Cooperative Society don damfari wani Favor Nnamani.

Laifin da ake tuhumar ta ya sabawa sashe na 1 (1) da 1 (3) na dokar damfara ta 2006, da sashe na 278 na dokar laifuka ta Legas 2011.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp