fidelitybank

Kotu na neman ‘yar kasuwa ruwa a jallo

Date:

Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Ikeja ta soke belin wata ‘yar kasuwa mai suna Blessing Adanu.

An dai gurfanar da Adanu ne bisa zargin damfarar wanda take karewa Naira miliyan 47.

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ce ta gurfanar da wanda ake tuhumar.

Tana fuskantar tuhume-tuhume biyu na samun kudi ta hanyar karya da kuma sata.

Wadda ake zargin ta ki amsa laifin da ake tuhumarta da shi a lokacin da aka gurfanar da ita a ranar 19 ga watan Disamba, 2019.

A yau ne mai shari’a Mojisola Dada ta janye belin ta tare da umurci hukumar EFCC da ta bayyana wanda ake nema ruwa a jallo.

Alkalin kotun ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 2 ga watan Disamba domin amincewa da rubutaccen adireshin karshe.

Lauyan EFCC, Samuel Daji ya ce shari’ar da aka shirya na karbar adireshin karshe ba za ta iya ci gaba ba saboda rashin halartar Adanu.

Don haka lauyan hukumar ya mika takardar bukatar kotun da ta janye belin.

Lauyan da ake kara, Olarenwaju Ajanaku bai yi adawa da bukatar masu gabatar da kara ba.

Ajanaku ya shaida wa alkalin cewa shi ma ya yi mamakin yadda wanda yake karewa bai zo kotu ba.

Ana tuhumar Adanu ne da yin kasuwanci a karkashin Emerald Multipurpose Cooperative Society don damfari wani Favor Nnamani.

Laifin da ake tuhumar ta ya sabawa sashe na 1 (1) da 1 (3) na dokar damfara ta 2006, da sashe na 278 na dokar laifuka ta Legas 2011.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp