Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Ikeja ta soke belin wata ‘yar kasuwa mai suna Blessing Adanu.
An dai gurfanar da Adanu ne bisa zargin damfarar wanda take karewa Naira miliyan 47.
Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ce ta gurfanar da wanda ake tuhumar.
Tana fuskantar tuhume-tuhume biyu na samun kudi ta hanyar karya da kuma sata.
Wadda ake zargin ta ki amsa laifin da ake tuhumarta da shi a lokacin da aka gurfanar da ita a ranar 19 ga watan Disamba, 2019.
A yau ne mai shari’a Mojisola Dada ta janye belin ta tare da umurci hukumar EFCC da ta bayyana wanda ake nema ruwa a jallo.
Alkalin kotun ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 2 ga watan Disamba domin amincewa da rubutaccen adireshin karshe.
Lauyan EFCC, Samuel Daji ya ce shari’ar da aka shirya na karbar adireshin karshe ba za ta iya ci gaba ba saboda rashin halartar Adanu.
Don haka lauyan hukumar ya mika takardar bukatar kotun da ta janye belin.
Lauyan da ake kara, Olarenwaju Ajanaku bai yi adawa da bukatar masu gabatar da kara ba.
Ajanaku ya shaida wa alkalin cewa shi ma ya yi mamakin yadda wanda yake karewa bai zo kotu ba.
Ana tuhumar Adanu ne da yin kasuwanci a karkashin Emerald Multipurpose Cooperative Society don damfari wani Favor Nnamani.
Laifin da ake tuhumar ta ya sabawa sashe na 1 (1) da 1 (3) na dokar damfara ta 2006, da sashe na 278 na dokar laifuka ta Legas 2011.