Isra’ila ta dage kan cewa tana bin dokokin kasa da kasa, bayan Kotun Majalaisar Dinkin Duniya ta bukaci dole ta gaggauta kawo karshen kisan kare dangi a Gaza.
Kotun hukukunta manyan laifuka ta ICJ da ke Hangue ta bada wannan umarnin ne a kan karar da Afirka Ta Kudu ta shigar, kan cewa Isra’ila na yiwa Falasdinawa kisan kare dangi.
Alkalan kotun dai ba su ambato Isra’ila ta dakatar da hare-harenta ba.
Sai dai sun dage kan cewa dole tayi duk mai yiwuwa wajen ganin ta ƙaurace kashewa ko jikkata fararan-hula, da hana haihuwa ko kuma jefe mutane Gaza cikin mawuyancin yanayi na rayuwa.