Wata kotun shari’ar Musulunci a jihar Kano, ta bayar da umarnin tsare wani mutum mai suna Yusha’u Ado mai shekaru 37 a gidan gyaran hali, bisa samunsa da laifin satar kwalin sinadarin girki.
Wanda ake tuhumar wanda ke zaune a Goron Dutse Quarters Kano, ya na fuskantar tuhuma guda biyu da suka hada da zamba cikin aminci da damfara.
Tun da farko, dan sanda mai shigar da kara, Sefara Abdullahi Wada, ya shaida wa kotun cewa, wanda ya shigar da karar, Jamilu Ibrahim na Galandanci Quarters, ya kai karar ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari a ranar 10 ga watan Maris.
Sefata Wada ya ce, wanda ya shigar da karar ya ruwaito cewa, ya baiwa Ado katan 260 sinadarin girki da ya ajiye a shagonsa, kuma a lokacin da ya je daukar kayansa ya gano cewa, kwalayen kayan guda 22 da kudinsu ya kai Naira 216,000 ya bata.
Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.