Kasar Ivory Coast ta shiga sahun kasashen Afirka da suka kawo karshen tilasta wa mutane amfani da takunkumi.
Kasar ta ce daga yanzu za a rika sanya takunkumin ne kawai a wuraren taron jama’a saboda raguwar masu kamuwa da cutar korona.
Har wa yau, ta ce mutanen da ke shiga kasar da wadanda ke halartar taruka ba sai sun nuna shaidar gwajin cutar ba.
Sabbin alkaluma da ke fitowa daga Ivory Coast din sun nuna cewa mutum tara ne ke kamuwa da cutar a rana, wanda ya tasamma mutum 796 da ke dauke da cutar a fadin kasar da ke Afirka ta Yamma.
Kawo yanzu, allura miliyan 10 aka shiga da su kasar, inda aka yi wa mutum miliyan huu rigakafi a kasar mai al’umma da ta haura miliyan 23. In ji BBC.