Kafofin yada labarai na gwamnatin Koriya ta Arewa sun sanar da cewa, kasar ta yi nasarar gwajin wani sabon makami, wanda ta ce zai inganta karfin sojin kasar.
Masana sun ce sun yi imanin cewa an ƙera sabon nau’in makami mai linzamin ne domin ɗaukar ƙananan makaman Nukiliya.
Sojojin Koriya ta Kudu sun tabbatar da cewa an harba makamai masu linzami biyu daga Arewa zuwa cikin teku a daren Asabar.
Masu aiko da rahotanni sun ce mai yiwuwa an yi gwajin ne dai-dai da zagayowar ranar da aka haifi Kim Il-sung, mutumin da ya kafa Koriya Ta Arewar.