Shugaban Koriya ta Kudu ya ce, zai ƙara inganta sojoji da ayyukan leƙen asiri a ƙasar bayan jirage marasa matuƙa biyar na Koriya Ta Arewa sun yi musu kutse.
Yoon Suk Yeol ya ce wannan lamari da ya faru ya nuna gazawa a irin shirin da sojojin ƙasarsa ke da shi.
Ya bayyana cewa Koriya Ta Kudu za ta samar da wani sashe na musamman na jirage marasa matuƙa.
Bayan kutsen da Koriya Ta Arewar ta yi da jiragen a jiya, sai takwararta Koriya Ta Kudu ta mayar da martani ta hanyar tashin jiragen yaƙi da masu saukar ungulu domin tunkarar jirage marasa matuƙan.
Sai dai rahotanni sun ce jiragen yaƙin sun yi harbi sama da sau 100 kan jirage marasa matuƙan Koriya Ta Arewa amma sun kasa kaɓo ko guda ɗaya.