Japan da Koriya ta Kudu sun ce Koriya ta Arewa ta sake yin gwajin wani makami mai linzami.
Ta yi gwajin ne a ranar Asabar, kamar yadda jami’an Japan da na Koriya ta Kudu suka bayyana.
A bikin sabuwar shekara, gwamnatin Pyongyang ta yi gwaji makamai da dama, na baya bayan nan shi ne wanda ta yi a ranar Asabar.
Tun a ranar Juma’a ma’aikatar harakokin wajen Amurka ta ce Koriya Ta Arewa na shirin gwajin makamin nukiliya.