Koriya ta Arewa ta harba wasu makamai masu linzami biyu na gwaji a cikin tekun Japan.
Makwabciyarta Koriya Ta kudu, ta ce wannan yunkuri ne na tunzuri.
Harba makaman na zuwa ne kwana guda bayan Amurka da Koriya ta Kudun sun gudanar da atisayen sojin hadin-gwiwa a matsayin jan-kunne kan irin wannan makami da aka harba a ranar Asabar.
Amurka ta ce atisayen shirin ne na kariya da tunkarar shirin nukiliyar Koriyar ta Arewa.
Sai dai shugaba, Kim Jong Un, na kallonsu a matsayin wani shirin maƙiya na mamaya.
Kanwarsa, Kim Yo Jong, tayi barazanar mayar da tekun wani sansanin daga muddin aka sake gudanar da irin wannan atisaye. In ji BBC.