fidelitybank

Komai ya daidaita a harin da ‘yan bindiga suka kai gidan yarin Kuje

Date:

‘Yan bindiga sun kai hari gidan yarin Kuje da ke unguwar Kuje a babban birnin tarayya Abuja a daren ranar Talata.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewa, ‘yan bindigar sun yi ta harbe-harbe ta kusan sa’a guda. Sun kuma bayyana cewa, an tashi bama-bamai a yayin harin.

Wata mai amfani da Twitter, Dara Moren, wadda ta ce, tana yankin a lokacin, ta yi wani rubutu game da harin.

“A yanzu haka a Kuje kuma an shafe kusan awa daya ana harbe-harbe. A ɗan kwantar da hankali kuma na gaba an sake fara harbe-harbe. Allah ya yi mana rahama,” kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter.

“An kai hari gidan yarin Kuje! Fashewar bama-bamai biyu, harbe-harbe marasa adadi,” wani mai amfani, J.S. Ramadan kuma ya wallafa a shafinsa na Twitter.

A wani labarin kuma, Ramadan ya yi zargin cewa fursunoni 15 ne suka tsere zuwa makarantar Sakandaren Gwamnati da ke yankin a yayin harin.

“Kimanin fursunoni 15 da suka fito daga gidan yarin Kuje ne suka kutsa cikin makarantar mu ta katanga. Dole ne mu kasance cikin sanyin gwiwa kuma mu ci gaba da yin addu’o’in neman lafiyarmu da kuma taimakon Allah mai yawa,” in ji Ramadan.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp