Kocin PSG Christophe Galtier na cikin matsala, bayan an yada kalamansa na nuna wariyar launin fata da kyamar Musulunci ga kafafen yada labarai.
Tsohon darektan kwallon kafa na OGC Nice Julien Fournier, a cikin imel, ya yi zarge-zarge a kan kocin Paris Saint-Germain, kuma ainihin imel ɗin ‘yan jarida Romain Molina da Daniel Riolo ne suka bayyana shi a ranar Talata.
Fournier ya aika imel ɗin zuwa INEOS (kamfanin da ke da Nice) darektan Dave Brailsford.
Sakon imel ɗin ya fallasa kalaman wariyar launin fata da Islama da Galtier ya yi a lokacin da yake a matsayin Manajan Nice, a cewar Sportskeeda.
Fournier, a cikin imel ɗin zuwa Brailsford, ya bayyana cewa, kocin ya bayyana rashin jin daɗin sa na samun ƴan wasa bakaken fata da musulmai da yawa a ƙungiyar.
“Ya (Christophe Galtier) ya gaya mani cewa dole ne in yi la’akari da ‘hakikanin birnin’ kuma ba za mu iya samun baƙar fata da Musulmai da yawa a cikin tawagar ba,” in ji imel a wani bangare.
Galtier ya kara bayyana a cikin sakon email din cewa, mutanen birnin Nice sun damu da cewa ‘yan wasa bakaken fata da musulmi ne suka karbe kungiyar duk da kasancewar birnin tsohon magajin garin Jacques Medecin, yana mai jaddada cewa, kungiyar ba ta nuna abin da mutane ke so ba. , “kamar yadda baya nuna kaina’.”
Tuni dai masu sha’awar kwallon kafa suka shiga shafukan sada zumunta suna yin Allah wadai da kalaman wariyar launin fata da kyamar Musulunci na Bafaranshen.