fidelitybank

Kocin Brazil ya ajiye aiki bayan ya sha kayi a Qatar

Date:

Kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Brazil, Tite, ya ajiye aikinsa bayan Croatia ta fitar da su daga Gasar Kofin Duniya a bugun finareti a wasan kwata fayinal da suka buga ranar Juma’a.

Kocin mai shekara 61, ya jagoranci Brazil tun daga 2016 kuma ya taɓa faɗa cewa zai bar aikin bayan gasar ta 2022 da ake yi a Qatar.

“Abin da ciwo amma na tafi ke nan. Ƙarshen lamarin ke nan a wajena,” kamar yadda ya faɗa wa ‘yan jarida bayan wasan da aka buga a filin wasa na Education City Stadium.

“Da ma na faɗi haka shekara ɗaya da ta wuce. Ban zo nan don na ci kofi ba kuma na ce zan ci gaba da aiki, waɗanda suka san ni sun san haka.”

Croatia ta doke Brazil 4-2 a bugun finareti bayan wasan ya tashi 1-1, inda ɗan wasa Neymar ya kamo Pele a yawan ci wa Brazil ƙwallaye da 75 kowannensu.

Akwai yiwuwar shi ma ɗan wasa Neymar ya jingine takalmansa saboda ya ce “babu tabbas ko zan sake buga wa Brazil wasa”.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
X whatsapp