fidelitybank

Ko da mutane sun ficce daga APC ita ce za ta yi nasara a zaben 2023 – Adamu

Date:

Biyo bayan sauya sheka da ‘ya’yan jam’iyyar All Progressives Congress mai mulki ke yi a baya-bayan nan, shugabanta na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce jam’iyyar ba za ta iya tilasta wa kowane dan jam’iyyar tsayawa ko ficewa ba.

Adamu, ya yi alfahari da cewa ko da mutane sun fice daga jam’iyyar, za ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa ya bayyana haka ne bayan ya ziyarci gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule a gidan gwamnati dake Lafia.

SaharaReporters ta ruwaito, tun a ranar Lahadi bayan da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu ya bayyana Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa, dan uwa musulmi ne wasu ‘yan jam’iyyar suka yi murabus daga mukaminsu.

Haka kuma an sha yin tofin Allah tsine a duk fadin kasar, musamman ma mabiya addinin kirista dangane da matakin da jam’iyyar ta dauka na gudanar da tikitin takarar shugaban kasa na musulmi da musulmi.

Sai dai Adamu ya ce, duk da cewa ba za su so kowa ya fice daga jam’iyyar ba, hakan ba zai hana kowa ba.

Ya ce, “Ba ma so mu rasa wani mamba amma idan da gangan dan mamba yana son ficewa daga jam’iyyar ba tare da neman mafita ba, ba za mu iya tilasta wa kowa ya tsaya ko barin jam’iyyar ba.

“Batun sauya sheka, akwai lokacinsa a siyasa musamman a kasashe masu tasowa, kuma ba sabon abu bane a Najeriya.

“Duk wanda yake cikin wannan jam’iyya babba ne kuma idan babba ya yanke shawara, to ko dai ka gamsar da shi, idan kuma hukuncin bai dace da kai ba, kuma ya aikata abin da ya umarta, to ka bar shi ga Allah shi ne ya tsara komai.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp