fidelitybank

Kishi Kummalon Mata: Wata ta jefa yaro mai shekaru 4 cikin rijiya a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Katsina ta kama Maryam Habibu, ‘yar shekara 18 da haihuwa, bisa zarginta da jefa ɗan kishiyarta mai shekaru hudu a cikin rijiya da ke karamar hukumar Kafur ta jihar.

Maryam Habibu waddat ta fito daga kauyen Leko da ke karamar hukumar Danja tare da wasu mutane 11 da ake tuhuma da laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami da satar shanu, an gurfanar da su a ranar Juma’a a hedikwatar ‘yan sanda da ke Katsina.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Gambo Isah, yayin da yake zantawa da manema labarai yayin holin ya bayyana cewa, an kama matar ne a ranar 9 ga Nuwamba, 2022.

Ya ci gaba da bayyana cewar ta fitar da yaron ne ta jefa shi cikin rijiya.

A cewar jami’in hulda da jama’a, Maryam Habibu da mahaifin wanda aka kashen sun kasance ba sa tare.

Maryam Habibu wanda ta zanta da manema labarai ta amince da aikata laifin, ta na mai cewa kaddara ce.

A cewarta, “Gaskiya ne na jefa yaron a cikin rijiyar da ya mutu amma an kaddara cewa zai mutu a ranar. Shi ya sa ya rasu.”

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp