Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo, ya kai wa mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ziyara dangane da kisan ƴan arewa 16 da wani gungun ƴansintiri ya yi a jihar a makon da ya gabata.
Mataimaki na musamman ga mataimakin shugaban majalisar dattawa a harkokin watsa labarai, Alhaji Isma’il Mudashir ya ce gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya je yi wa Barau Jibrin gaisuwar rasuwar farautan guda 16 kasancewar shi ma ɗan jihar Kano ne.
Gwamna Okpebholo ya shaida wa Sanata Barau Jibrin cewa gwamnatin jihar za ta sha alwashin tallafa wa iyalan mutanen da aka kashe.
Daga ƙarshe gwamnan ya shaida wa Sanata Barau Jibrin cewa gwamnatinsa za ta yi duk abin da za ta yi wajen ganin an hukunta duk waɗanda ke da hannu a wannan al’amari.