fidelitybank

Kisan Sarkin Gobir rashin imani ne da rashin tausayi – Gwamnan Sokoto

Date:

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu ya miƙa ta’aziyarsa a kan rasuwar Hakimin Gatawa Alhaji Isa Muhammed Bawa, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane.

A saƙon jajen, gwamnan ya ce yana miƙa saƙon jajensa zuwa ga iyalan marigayin da mutanen Sabon Birni da dukkan mutanen jihar.

Cikin wata sanarwa da Sakataren Watsa Labaransa, Abubakar Bawa ya fitar, Aliyu ya ce gwamnatinsa ba za ta huta ba har sai an kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Gwamna Aliyu ya bayyana kisan a matsayin “rashin tausayi da dabbanci”, wanda dole a yi Allah-wadai da shi.

Sanarwar ta bayyana mamacin a matsayin mai gaskiya da amana, da son zaman lafiya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen aiki ga al’umma.

Dokta Aliyu ya yi kira ga jami’an tsaro a jihar da su ƙara ƙoƙari a kan wanda suke yi domin tabbatar da tsaro a jihar, sannan su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa an kama waɗanda suka kashe hakimin domin su fuskanci hukunci.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp