fidelitybank

Kisan Matashi: Ba za mu iya jure irin mummunan aikin ba – Kungiyar Miyetti

Date:

Kungiyar Miyetti Allah ta Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) ta tabbatar da harbe wani makiyayi dan shekara 14 mai suna Idris Idris a unguwar Dong da ke karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato.

A cewar shugaban kungiyar na jihar, Malam Nura Abdullahi, ya ce an kashe marigayin ne da yammacin ranar Asabar.

Ya ce“An kai masa hari ne a lokacin da yake kiwon dabbobi, amma ba a kashe saniya ba ko daya ba. Lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:pm. Makiyayan biyu ne, amma daya ya tsira daga harin. Mun kai rahoto ga DPO na shelkwatar ‘yan sandan karamar hukumar Bassa.

“Babu hujjar kisan, saboda mamacin ya na kiwon shanu ne kawai. Me ya yi da ya cancanci a kashe shi? Ba za mu iya ci gaba da jure wa irin wannan mummunan aiki ba. Muna kira ga jami’an tsaro da su yi abin da ya dace a kai, domin kamo wadanda suka aikata wannan aika aika.” In jiNura Abdullahi.

Mun kuma tuntubi mai magana da yawun rundunar ’Yan sandan Jihar, ASP Ubah Gaberiel, game da faruwar lamarin, bai amsa kiran da wakilinmu ya yi masa ba.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp