Kungiyar Miyetti Allah ta Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) ta tabbatar da harbe wani makiyayi dan shekara 14 mai suna Idris Idris a unguwar Dong da ke karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato.
A cewar shugaban kungiyar na jihar, Malam Nura Abdullahi, ya ce an kashe marigayin ne da yammacin ranar Asabar.
Ya ce“An kai masa hari ne a lokacin da yake kiwon dabbobi, amma ba a kashe saniya ba ko daya ba. Lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:pm. Makiyayan biyu ne, amma daya ya tsira daga harin. Mun kai rahoto ga DPO na shelkwatar ‘yan sandan karamar hukumar Bassa.
“Babu hujjar kisan, saboda mamacin ya na kiwon shanu ne kawai. Me ya yi da ya cancanci a kashe shi? Ba za mu iya ci gaba da jure wa irin wannan mummunan aiki ba. Muna kira ga jami’an tsaro da su yi abin da ya dace a kai, domin kamo wadanda suka aikata wannan aika aika.” In jiNura Abdullahi.
Mun kuma tuntubi mai magana da yawun rundunar ’Yan sandan Jihar, ASP Ubah Gaberiel, game da faruwar lamarin, bai amsa kiran da wakilinmu ya yi masa ba.