Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya kira hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza da ”kisan kiyashi”.
Yayin da yake jawabi cincirindon mutane a birnin santambul, Mista Erdogan ya ce ƙasashen yamma ƙawayen Isra’ila su ne ke ingizata wajen aikata abin da ya kira “laifukan yaƙi”.
“Isra’ila, za mu ayyana ki a matsayin mai aikata laifukan yaƙi a duniya. Muna shirin yin haka, kuma za mu gabatar da Isra’ila ga duniya a matsayin mai aikata laifukan yaƙi”, in ji Erdogan.
Shugaban na Turkiya ya ci gaba da kare matsayinsa na ƙin amincewa da ayyana Hamas a matsayin “ƙungiyar ta’addanci”.
Matsayin da ƙasashen Amurka da Birntaniya da wasu wuraren suka ɗauka kan ƙungiyar.
Erdogan na jawabin ne a gaban taron ɗimbin jama’a da ya ce sun kai mutum miliyan 1.5
Waɗanda suka halarci taron sun riƙe tutar Falasdinawa da ta ƙasar Turkiya.
Taron – wanda aka kira babban tattakin goyon bayan Falasɗinawa – an gudanar da shi ne a filin jirgin sama na Ataturk, inda Erdogan ke gudanar da gangaminsa a baya-bayan nan.
A ranar Asabar, ya sake nanata sukarsa ga ƙasashen Yamma, kan ƙin kiran tsagaita wuta a Gaza.
Shugaban na Turkiyya ya kuma kira ƙasashen musulmai na duniya da su haɗa kai.