fidelitybank

Kisan kiyashi Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa zan ayyana ku a matsayin yaƙi ƙarara – Turkiyya

Date:

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya kira hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza da ”kisan kiyashi”.

Yayin da yake jawabi cincirindon mutane a birnin santambul, Mista Erdogan ya ce ƙasashen yamma ƙawayen Isra’ila su ne ke ingizata wajen aikata abin da ya kira “laifukan yaƙi”.

“Isra’ila, za mu ayyana ki a matsayin mai aikata laifukan yaƙi a duniya. Muna shirin yin haka, kuma za mu gabatar da Isra’ila ga duniya a matsayin mai aikata laifukan yaƙi”, in ji Erdogan.

Shugaban na Turkiya ya ci gaba da kare matsayinsa na ƙin amincewa da ayyana Hamas a matsayin “ƙungiyar ta’addanci”.

Matsayin da ƙasashen Amurka da Birntaniya da wasu wuraren suka ɗauka kan ƙungiyar.

Erdogan na jawabin ne a gaban taron ɗimbin jama’a da ya ce sun kai mutum miliyan 1.5

Waɗanda suka halarci taron sun riƙe tutar Falasdinawa da ta ƙasar Turkiya.

Taron – wanda aka kira babban tattakin goyon bayan Falasɗinawa – an gudanar da shi ne a filin jirgin sama na Ataturk, inda Erdogan ke gudanar da gangaminsa a baya-bayan nan.

A ranar Asabar, ya sake nanata sukarsa ga ƙasashen Yamma, kan ƙin kiran tsagaita wuta a Gaza.

Shugaban na Turkiyya ya kuma kira ƙasashen musulmai na duniya da su haɗa kai.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp